Za a samu ruwan sama a kusan dukkan jihohin Najeriya a yau Juma’a – NiMet

👍 Ku bi shafinmu na Facebook

Don karanta labaran mu kai-tsaye a Facebook

Hukumar Kula da Yanayi ta Najeriya (NiMet) ta sanar da cewa za a samu ruwan sama mai haɗuwa da guguwar iska a sassa daban-daban na ƙasar nan ranar Juma’a, 19 ga Satumba 2025.

Wakiliyarmu ta tattaro daga rahoton NiMet cewa za a samu ruwan sama da guguwar iska a wasu sassan Taraba da safe, yayin da da yamma ake sa ran samun hadari mai ɗauke da iska da ruwan sama a Adamawa, Bauchi, Kaduna, Taraba, Gombe, Kano, Jigawa, Borno da Yobe.

Hasashen ya nuna cewa za a fara da yanayi mai ɗan sanyi tare da hasken rana, sai dai daga baya ana sa ran ruwan sama mai yawa a yawancin sassan yankin.

A yankin Kudu kuma, NiMet ta bayyana cewa za a samu ruwan sama marar yawa da safe a Cross River da Akwa Ibom, sannan daga baya ana sa ran samun hadiri mai ɗauke da iska da ruwan sama a mafi yawan sassan kudu.

NiMet ta ja hankalin jama’a cewa ruwan sama zai iya kawo tsaiko a harkokin waje, kuma direbobi su yi taka-tsantsan saboda matsalar rashin gani sosai dalilin duhun hanya.

Haka kuma ta shawarci mazauna yankunan da ke fuskantar ambaliyar ruwa da su ɗauki matakan kariya.

👍 Ku bi shafinmu na Facebook

Don karanta labaran mu kai-tsaye a Facebook

Leave A Reply

Your email address will not be published.