ADC ta zargi APC da kai hari coci a Lagos saboda tsoron shaharar da take samu
Jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ta zargi jam’iyyar APC mai mulki da tsoratarwa da tayar da hankali bayan harin da aka kai wurin taronta a wani coci a Alimosho, Jihar Lagos.
Wakilinmu, Faruk Ahmad, ya tattaro daga wata sanarwa da mai magana da yawun ADC, Malam Bolaji Abdullahi, ya wallafa a dandalin X a ranar Lahadi, yana cewa, “APC na jin tsoron shaharar ADC a faɗin ƙasa, kuma matakin da suka iya ɗauka shi ne na tayar da hankali da tsoratarwa.”
Ya ƙara da cewa: “Harin da aka kai jiya a coci inda ake gudanar da taron ADC a Alimosho sabon tabo ne, yana mai nuna cewa APC ba ta daraja ko da Coci ba.”
Jam’iyyar ta kuma zargi APC da amfani da ƴan sanda a matsayin rundunar Gestapo na jam’iyya mai mulki ta APC, abin da ta ce na haifar da barazana ga dimokuraɗiyya da ƴancin siyasa a ƙasar.